Posts

Showing posts from November, 2017

HANYOYIN TARBIYA(4)

3.Tarbiyantar da yaro a kan kyawawan halaye: Lallai tarbiyantar da yaro a kan dabiu na kwarai yana daga cikin abunda addinin musulunci ya yi umurni da shi saboda muhimmancin hakan ga mutum da kuma rayuwar alumma. Samar da 'ya'ya na gari ya kan samar da ci gaba ga alumma da kuma  samun makoma mai kyau ga wanda ya sifantu da su. Siffantuwa da kyawawan halaye abu ne mai girma wanda dalilin hakan Allah madaukakin sarki ya yabi Annabinsa(SAW) a kuraninsa mai tsalki inda yake cewa:"وانك لعلى خلق عظيم"fassara "lallai kana a kan halaye masu girma" wato kyawawan halaye. Haka Annabi(SAW) yana cewa a cikin hadisi:"بعثت لأتمم مكارم الاخلاق" fassara "an aiko ni don in cika kyawawan halaye". Wato kyawawan dabiu su ne babban sakon da musulunci yake dauke da shi. Shi ya sa yake daga cikin alamar musulmi na kwarai siffantuwa da halaye na kwarai. Addinin musulunci gaba dayan shi yana misaltuwa ne a cikin kyawawan dabiu kuma imani kansa yana bayyna ta hany...

HANYOYIN TARBIYA(3)

2. Ba wa yaro nagartaccen ilimi: Allah madaukakin sarki a cikin kuraninsa mai tsalki yana cewa"هل يستوي الذين يعلمون والذين لا يعلمون" fassara "shin wadanda suke da  ilimi suna dai dai da wadanda ba su da shi" tabbas ba za su yi daidai ba. Ilimi shi ne mabudin rayuwa duk girman mutum da hankalinsa in ba ya da ilimi za ka ga yana da nakasu(tawaya). To shi ya sa kai me tarbiya za ka jajirce don dora yaronka akan hanyar neman ilimi tun yana karami. Ka samar mishi makaranta ta kwarai wacce take bada nagartaccen ilimi da nagartacciyar tarbiya. Dole ne ka kula da hannun wa za ka danka yaronka. Wasu iyaye saboda kwadayin yaro ya koyi turanci za ka ga sun kai shi makarantar arna inda baa ma kula da addini ba balantana kuma tarbiyarsa.koyon yare irin turanci da wasu yaruka yana da babban amfani ga mutum kamar yanda Annabi (SAW) ya kwadaitar amma sai mutum ya bi ta hanyar da ta dace wacce zai kare yaronsa daga koyon wata akida wacce ba ta dace da akidar musulunci ba.   Ilim...

HANYOYIN TARBIYA(2)

Karkashin dasa kyakkyawar akidah ga yaro,kamar yanda muka sani cewa son Allah yana tare da son Annabi (SAW) ne don haka kai mai tarbiya ka sani cewa dole ne ka cika zuciyar yaronka da son Annabi(SAW). Saboda son Annabi (SAW)yana cikin cikar imani. Annabi (SAW) ya ce"لا يؤمن احدكم حتى اكون احب اليه من والده وولده والناس اجمعين" fassara,"Imanin dayanku ba zai cika ba har sai na kasance nine mafi soyuwa gare shi akan 'ya'yansa da mahaifansa kai da ma mutane gaba daya. To amma ta wace hanya za mu bi mu dasa son Annabi(SAW)a cikin zukatan 'ya'yanmu. 1. Karantar da su tarihin Annabi(SAW) da yi musu bayanin cewa an aiko shi ne don fitar da mu daga duhun jahilci zuwa ga shiriya kuma shi rahama ne gare mu kamar yanda kurani ya yi bayani. 2. Fitar musu da halayen Annabi(SAW) daga tarihinsa da kurani da yi musu bayanin shi ne mafificin halitta don haka shi ne abun koyi a gare mu. 3. Yi musu bayani a kan muujizojinsa 4. Yi musu bayani a kan muamalarsa da yara da taus...

HANYOYIN TARBIYA(1)

HANYOYIN DA SUKA DACE KA DORA YARONKA AKANSU DON KYUTATA TARBIYARSA DASA SHI A KAN AKIDA TA KWARAI:   Annabi(SAW) yana cewa “ما من مولود إلا يولد على الفطرة فأبواه يهودانه أو ينصرانه أويمجسانه” Fassara:”ba wani yaro da ake haihuwa face yana akan fidrah(akidah ta kwarai) sai dai iyayensa su maida shi bayahude ko kirista ko bamaguje” Da wannan hadisi ne nake cewa ya kai mai tarbiya dole ne ka jajirce wurin kiyaye wannan fidrah da yaro ya akanta,don idan ka yi sake har ya fada zuwa ga wata mummunar akidah to lallai Allah zai tambaye ka ranar lahira. Annabi(SAW) yana cewa:”كلكم راع وكلكم مسؤول عن رعيته” Fassara:”dukkaninku makiyaya ne kuma kowannenku zaa tambaye shi akan abun kiwonsa”. Wace hanya ce ya kamata ka bi kai mai tarbiya don dasa yaronka a kan akida ta kwarai? Tun farko dai ya wajaba samo masa uwar kwarai wacce ta ginu akan karantarwa ta addini sannan kuma ta koshi da akida ta kwarai Dole ne kiyaye ladubban kwanciya(jimaii) da gabatar da shi akan ka...

GABATARWA

Gabatarwa Allah madaukakin sarki a cikin kuraninsa mai tsalki ya siffanta mana yara yana mai cewa “المال والبنون زينة الحياة الدنيا” fassara “dukiya da ‘ya’ya su ne kawar rayuwar duniya. Zamu tabbatar da haka ne idan muka yi laakari da irin farin ciki da tasirin da yara su ke bar mana a cikin zukatanmu lokacin da suke abubuwan ban dariya na nuna halin kurciya har dai lokacin da suke kanana. Mutum ba zai iya gane haka ba sai lokacin da ya nisanta da su. Don haka ka sani cewa kyautar ‘ya’ya daga Allah niima ce baba da ya maka,ya zama dole ka yi aiki tukuru don dora wannan niimar akan hanyar da ta dace,hanyar da Allah yake so,don zai tambaye ka akan ta ranar kiyama. Mai karatu biyo ni a hankali don samun haske a kan hanyoyin da suka dace ka dora yaranka a kansu don samun kyakkyawan iri da zaka yi alfahari da shi anan duniya kuma ka samu babban rabo a gobe kiyama.